An Ga Jaririn Watan Ramadana A Saudiyya
Daga Muhammad Kaka Misau
![](https://i0.wp.com/baushetimes.com/wp-content/uploads/2022/04/wp-1648828902045.jpg?w=800&ssl=1)
Hukumomi a kasa mai tsarki ta Saudiyya sun sanar da cewa, an samu ganin jaririn watan ramadana a yankuna da dama, don haka gobe Asabar ne zai kasance ranar daya ga watan Ramadana.
Kafofi daga kasar Saudiyya sun tabbatar da hakan, inda tunin al’ummar Musulmai suka fara shirye-shiryen daukan Azumin watan Ramadana a goben.
Allah ya sa a fara a sa’a a kammala a sa’a, kuma muna fatan Allah amshi ibadodinmu.