Da Diminsa: Mataimakin Kakakin Majalisar Bauchi Ya Sha Kaye A Zaben Fid Da Gwani
![](https://i0.wp.com/baushetimes.com/wp-content/uploads/2022/05/FB_IMG_1653239020152.jpg?w=800&ssl=1)
Daga Khalid Idris Doya
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin jihar Bauchi, Honorable Danlami Ahmed Kawule ya sha kasa a zaben fitar da gwani na Dan Majalisar tarayya mai neman wakiltar mazabar karamar hukumar Bauchi a karkashin jam’iyyar PDP da ke mulki a jihar.
Wakilinmu ya labarto mana cewa Alhaji Aminu Ali Garu shine ya kada Kawule da gagarumar nasara bayan fafata zaben da aka gudanar ta hanyar amfani da wakilai wato (delegates) a yau Lahadi a Bauchi.
Da ya ke bayyana farin cikinsa bisa wannan nasarar, Aminu Garu ya gode wa Allah bisa samun nasara da ya yi, ya kuma gode wa delegates bisa amincewa masa da zabinsa.
![](https://i0.wp.com/baushetimes.com/wp-content/uploads/2022/05/FB_IMG_1653239043855-685x1024.jpg?resize=685%2C1024&ssl=1)
Ya kuma yi kira ga wadanda suka fafata neman kujerar tare da su wato sauran mutum biyun da suka fadi da su hada hannu wajen samun nasarar jam’iyyar a babban zaben 2023 da ke tafe.
Duk kokarin da ‘yan jarida suka yi don jin ta bakin Kawule bisa wannan shan kayen da ya yi abun ya citura zuwa yanzu.
![](https://i0.wp.com/baushetimes.com/wp-content/uploads/2022/05/FB_IMG_1653238981465.jpg?w=800&ssl=1)
Wakilinmu ya nakalto cewa, shi dai mataimakin Kakakin Majalisar yanzu haka shine ke wakiltar mazabar Zungur, Galambi da Miri a Majalisar wakilai ta jihar, wanda tunin kuma jam’iyyar ta zabi wani a kan wannan kujerar da zai daga mata tutarta na neman wannan mazabar a zaben 2023.