Gwamnatin Tarayya Ayyana Ranakun Laraba Da Alhamis Don Hutun Babbar Sallah
![](https://i0.wp.com/baushetimes.com/wp-content/uploads/2023/06/download.jpeg?resize=216%2C233&ssl=1)
Daga Khalid Idris Doya
Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Laraba 28 ga watan Yuni da Alhamis 29 ga watan Yuni a matsayin ranakun hutun Babbar Sallah.
Hakan na kunshe ne ta cikin sanarwar da babban Sakataren ma’aikatar kula da harkokin cikin gida, Oluwatoyin Akinlade ya fitar a ranar Litinin.
Sanarwar ta ce, “Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Laraba da Alhamis a matsayin ranakun hutun Babbar Sallar Layya.”
Gwamnatin ta taya al’ummar musulmi a Nijeriya da ‘yan Nijeriya mazauna kasashen waje murna bisa zagayowar Idin Layya tare da fatan za a yi bukukuwa cikin koshin lafiya.
“Muna fatan al’ummar musulmi za su addu’o’in a lokutan bukukuwan ga cigaban zaman lafiyar kasa da bunkasar ciki mai daurewa. Muna fatan a yi bukukuwa lafiya,” sanarwar ta ce.